A jamhuriyar Nijar dan takarar jam’iyyar MDR TARNA a zaben shugaban kasa na 2016 Dr. Adal Rhubeid ya karyatar da wasu rahotannin da aka bayar akansa a kwanakin baya cewa yana tunzura matasa abzinawa su dauki makamai da nufin yiwa gwamnati tawaye.
Ranar 3 ga watan Oktoba ta kowace shekara ce Majalisar Dinkin Duniya ko MDD ta kebe a matsayin ranar muhalli ta duniya, ranar da ake kara jaddada muhimmancin muhalli
Wani buki na al’ada da aka saba gudanarwa kowace shekara a kasar Ethiopia ya haddasa mutuwar mutane masu yawa jiya lahadi, a lokacin da ‘yan sanda suka harba barkonon tsohuwa tare da yin harbi da harsasai a sama don kashedi ga masu zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati.
Biyo bayan yawan hare-haren da kungiyar Boko Haram ke kaiwa yankin Arewa Mai Nisa a jamhuriyar Kamaru rayuwa ta soma yiwa mazauna yankin wuya saboda harkokin yau da kullum na durkushewa inda ko kasuwanci ma ya gagara sanadiyar rashin tsaro
Kungiyar ta kai harin ne a harabar wani gidan cin abinci mai farin jini ga farar hula da jami'an tsaro duka.
Ministan shari’a a Sudan ta Kudu, ya musanta zargin da wadanda suka fice daga yankin Jebel Marra da ke Dafur ke yi na cewa, gwamantin kasar ta yi amfani da sinadari mai guba akansu.
Damuwa da irin yadda ilimin yara a jamhuriyar Nijar ke kara tabarbarewa ya sa hukumar dake da alhakin kula da ilimi kafa kwamitin mutane ishirin da zummar neman mafita.
Ministan shari’a a Sudan ya musunta maganar da yan gudun hijira a Jabel Marra ta yankin Darfur suka yi na cewa sun shaki iskar wani sanadari mai guba a hannun gwamnatin Sudan din.
Gwamnatin Somalia ta bukaci bayanai daga Amurka a kan farmakin da ta kai ta sama a ranar Laraba a tsakiyar Somalia.